‘Yan uwan wadanda suka mutu a hatsarin jirgin saman sun hallara  a babban filin tashi da saukar jiragen sama na babban birnin kasar, Lilongwe, domin tarban gawarwakin a yammacin ranar Talata. Hoto / Gwamnatin Malawi       

Gwamnatin Malawi ta ayyana kwanaki 21 na makoki a fadin ƙasar don girmama mataimakin shugaban ƙasar Saulos Chilima da wasu mutane takwas da suka mutu a hatsarin jirgin sama.

Da safiyar ranar Litinin ne jirgin sojin da ya ɗauko mataimakin shugaban ƙasar da tawagarsa ya yi ɓatan-dabo, bayan da ya gaza sauka saboda rashin kyawun yanayi.

Jirgin ya tashi ne daga babban birnin ƙasar Lilongwe zuwa Mzuzu wanda ke da tazarar kilomita 230, inda za a yi jana’izar wani tsohon ministan ƙasar.

An tsinci sauran tarkacen jirgin ne a ranar Talata a cikin wani babban daji mai tsaunuka da ke kusa da garin Mzuzu.

An soma makoki na ƙasa baƙi ɗaya ne daga ranar Talata 11 ga watan Yuni zuwa ranar Litinin 1 ga watan Yuli, kamar yadda majalisar ministocin ta bayyana a cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Talata.

Yin ƙasa da tutar ƙasar

Shugaban ƙasar Lazarus Chakwera ya ba da umarni a yi ƙasa-ƙasa da tutar ƙasar a ko ina a fadin ƙasar har tsawon lokacin makokin.

Majalisar ministocin ƙasar ta ce daga baya za a fitar da cikakken bayani game da lokacin da za a yi jana'izar waɗanda suka mutu a hatsarin.

An kai gawar Chilima da 'yan tawagarsa da suka mutu zuwa babban birnin ƙasar Lilongwe.

Shugaba Chakwera ya samu rakiyar ministocin gwamnati da wasu jami'ai domin karɓar gawawwakin a filin jirgin saman Kamuzu a yammacin ranar Talata.

Manyan shugabannin duniya sun yi ta miƙa saƙon ta'aziyyarsu ga iyalai da kuma gwamnatin ƙasar ta Malawi.

The Zambian Air Force helicopter carrying the body of Vice President Dr Saulos Chilima arrived in Lilongwe through...

Posted by Malawi Government on Tuesday, June 11, 2024
TRT Afrika