An yi ta ɗaga tutucin Rasha a yayin zanga-zanga a sassan Nijeriya. / Hhoto: Getty Images

Jami’an diflomasiyyar Poland a ranar Juma’a sun yi kira da a saki ‘yan kasar bakwai da ake tsare da su a Nijeriya, abin da Warsaw ke ganin rashin fahimta ne a yayin zanga-zangar da ake yi a kasar da ke Yammacin Afirka.

A farkon makon ne aka tsare wasu dalibai shida ‘yan kasar Poland da wani malami daga Jami’ar Warsaw, wadanda ke halartar wani shiri na nazarin harshen Hausa a jihar Kano da ke arewacin Nijeriya.

Wani mai magana da yawun hukumar leƙen asirin Nijeriya ya ce an kama su ne da laifin ɗaga tutocin kasar Rasha yayin zanga-zangar, abin da jami'an kasar Poland suka ce ba zai yiwu ba.

Mataimakin Ministan Harkokin Wajen Ƙasar Jakub Wisniewski ya roƙi Najeriya da ta kyale daliban da malamin su koma gida ga iyalansu, inda ya yi wa manema labarai karin haske kan kokarin da kasar Poland ke yi kan lamarin bayan ganawa da mai kula da harkokin Nijeriya a Warsaw.

'Jahiltar al'adu'

“A yayin taron, na bayyana cewa na gamsu da cewa halayen daliban na iya haifar da rashin sanin al’adu da dokokin yankin. Na roki yiwuwar mayar da su Poland, zuwa gidajensu, inda iyalansu ke jiransu, ”in ji Wisniewski.

Wisniewski ya ce bai yarda daliban sun ɗaga tutocin kasar Rasha ba.

Ba kasafai ake samun masu ra'ayin goyon bayan a kasar ta Tsakiyar Turai ba, wacce ke da mummunan tunanin shan wahala a karkashin mulkin Rasha a baya. Al'ummar Poland a yau suna matukar sukar ta'addancin Rasha a Ukraine kuma suna mara wa Ukraine baya sosai.

Wisniewski ya ce an kai ‘yan ƙasar ta Poland bakwai zuwa babban birnin tarayya Abuja, kuma suna cikin koshin lafiya. An shirya jakadan Poland zai gana da su a yammacin Juma'a.

Haramta zanga-zanga

Wisniewski ya yi nuni da cewa, a halin yanzu akwai dokar hana fita da kuma haramta zanga-zanga a Nijeriya, inda ake gudanar da gagarumar zanga-zanga a cikin al'ummar kasar miliyan 220 sakamakon hauhawar farashin kayayyaki da yunwa.

An ga wasu ‘yan Nijeriya masu zanga-zanga suna daga tutocin kasar Rasha a jihohin arewacin kasar, suna ci gaba da yin wani irin yanayi da ake gani a Afirka a kasashen da aka yi juyin mulki, inda masu ra’ayin Rasha ke kara ta’azzara yayin da gwamnatocin soja suka yanke alaƙa da Ƙasashen Yamma.

AP