| Hausa
AFIRKA
2 MINTI KARATU
Kotun Nijar ta cire wa Bazoum Mohamed rigar kariya
Hukumomin sojin Nijar suna zargin Bazoum da cin amanar ƙasa da ɗaukar nauyin 'yan ta'adda da kitsa tuggu ga ƙasar.
Kotun Nijar ta cire wa Bazoum Mohamed rigar kariya
A watan Yulin 2023 ne sojoji suka kifar da gwamnatin Mohamed Bazoum kuma tun wancan lokacin yake tsare./Hoto: Reuters / Others

Babbar kotun Jamhuriyar Nijar ta cire wa hamɓararren shugaban ƙasar Mohamed Bazoum rigar kariya, a wani mataki da ake gani zai bayar da ƙofa a tuhume shi tun bayan kifar da gwamnatinsa.

"An bayar da umarni a cire wa Mohamed Bazoum rigar kariya," a cewar kotun wadda sojoji suka kafa a watan Nuwamba.

Hukumomin sojin Nijar suna zargin Bazoum da cin amanar ƙasa da ɗaukar nauyin 'yan ta'adda da kitsa tuggu ga ƙasar.

Bazoum na tsare a hannun hukumomin sojin Nijar tun da suka yi masa juyin mulki a watan Yulin shekarar 2023.

A watan Agusta, sojojin ƙasar sun sanar da cewa za su tuhume da da laifukan "cin amanar ƙasa da yin ƙafar-ungulu ga tsaron Nijar".

A shekarar 2021 aka zaɓi Bazoum a matsayin shugaban Nijar bayan kammala wa'adin mulkin shekaru takwas na Mahamadou Issoufou, inda ya kasance shugaban farko na farar-hula da ya miƙa mulki ga wani shugaban na farar-hula.

A watan Janairu ne wata kotun soji a Jamhuriyar Nijar ta saki Salem, ɗan Mohamed Bazoum, wanda aka tsare su tare da kuma mai ɗakinsa.

MAJIYA:TRT Afrika