Gwamnatin jihar a ce an gudanar da rusau din ne domin yin kwaskwarima ga ginin majalisar. / Hoto: Others

Rahotanni daga Jihar Ribas da ke kudu maso kudancin Nijeriya na cewa an rushe ginin majalisar dokokin jihar da ke Fatakwal babban birnin jihar.

An gudanar da rusau din ne a daidai lokacin da gwamnan jihar Siminalayi Fubara yake gabatar da kasafin kudin 2024 a gidan gwamnatin jihar ga Kakakin Majalisar Jihar Edison Ehie da makarrabansa.

A ranar Talata ne Kotun Jihar Ribas ta tabbatar da Edison Ehie, wanda abokin gwamnan jihar ne a matsayin halastaccen kakakin majalisar.

Wasu daga cikin kafofin watsa labarai na Nijeriya sun wallafa bidiyon motocin buldoza da ke rugurguza ginin.

Sai dai a sanarwar da kwamishinan watsa labarai na jihar Joseph Johnson ya fitar, ya ce ya zama tilas gwamnati ta yi kwaskwarima ga ginin majalisar sakamakon gobarar da ta faru a ranar 30 ga watan Oktoba.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ake kara samun tsamin dangantaka tsakanin gwamnan Jihar Ribas Siminalayi Fubara da kuma tsohon gwamnan jihar Nyesom Wike.

TRT Afrika