Gidan rediyon da aka rufe sakamakon dalilin tsaron ƙasa shi ne Gumah FM da ke a Bawku. / Hoto: Getty Images

Ministan Sadarwa da Fasahar Zamani na Ghana, Samuel Nartey George, ya bayar da umarni a rufe gidajen rediyo bakwai a ƙasar kan dalilan tsaron ƙasa da saɓa ƙa’idojin watsa labarai.

A umarnin da ministan ya bayar a ranar Talata, 18 ga Fabrairun 2018, ya buƙaci Hukumar Sadarwa ta Ghana ta aiwatar da umarnin nan take ga gidajen rediyon da lamarin ya shafa.

A wani saƙo da ministan ya wallafa a shafinsa na X, ya bayyana cewa an rufe gidan rediyo ɗaya bisa dalili na tsaro sai kuma gidajen rediyo shida kan dalilin watsa shirye-shirye a kan mitocin rediyo waɗanda ba a amince da su a hukumance ba waɗanda aka gano bayan binciken da aka gudanar.

Gidan rediyon da aka rufe sakamakon dalilin tsaron ƙasa shi ne Gumah FM da ke a Bawku.

Sai kuma gidajen rediyon da aka rufe bisa dalilin saɓa ƙa’ijojin watsa labarai sun haɗa da Fire Group of Companies da ke Sunyani mai watsa shirye-shirye kan 90.1MHz, sai Zar Consult Limited da ke Tamale mai watsa shirye-shirye kan 89.7MHz.

Haka kuma akwai Abochannel Media Group da ke Adidome mai watsa shirye-shirye kan 105.7MHz da Okyeame Radio Limited da ke Bibiani mai watsa shirye-shirye kan 99.7MHz sai kuma Mumen Bono Foundation da ke Techiman mai watsa shirye-shirye kan 99.7MHz da kuma Osikani Community FM da ke Nkrankwanta mai watsa shirye-shirye kan 99.7MHz.

Ya bayyana cewa bayan dakatar da gidajen rediyon, za a ɗauki mataki a kansu nan ba da jimawa ba.

Ministan ya kuma ƙara jaddada aniyarsa ta ƙara sa ido kan watsa shirye-shirye tare da buƙatar duka kafafen watsa labarai su bi ƙa’idojin da aka gindaya musu.

TRT Afrika
Muna amfani da ka’idojin yanar gizo. Muna son ku san cewa idan kuka ci gaba da amfani da wannan shafin, kun amince da wadannan ka’idojin.Ka’idoji
Na amince