| Hausa
TURKIYYA
2 MINTI KARATU
Turkiyya ta ceto daruruwan bakin-haure da Girka ta kora
Jami’an tsaron gabar Tekun Turkiyya sun ceto bakin-haure sama da 270 wadanda Girka ta kora a yankin ruwan Turkiyya, kungiyoyin kare hakkin dan'adam na kasa da kasa na ci gaba da suka kan haramtaccen matakin na mahukuntan Girka.
Turkiyya ta ceto daruruwan bakin-haure da Girka ta kora
Turkiyya da kungiyoyin kare hakkin duniya sun sha yin Allah wadai ga haramtaccen matakin da kasar Girka ke dauka na korar bakin haure ba bisa ka'ida ba. / Hoto: AA / Others
25 Agusta 2023

Jami'an tsaron gabar Tekun Turkiyya sun ceto bakin-haure sama da 270 da suka saba ka'ida bayan da hukumomin Girka suka kora su yankin ruwan Turkiyya ba bisa ka'ida ba.

A wata sanarwar da ta wallafa a shafinta na intanet, rundunar tsaron gabar tekun Turkiyya ta bayyana cewa, ta ceto bakin-haure 140 wadanda ke tafe ba bisa ka'ida ba a cikin Tekun Aegean, bayan mayar da kwale-kwalensu da hukumomin Girka na yankin Bodrum da Dalaman suka yi zuwa Tekun Birnin Mugla.

Kazalika, sashen jami'an tsaron gabar tekun sun kubutar da jumullar bakin-haure 57, daga cikin wani kwale-kwalen roba a gabar tekun yankunan Dikili da Cesme da ke yammacin lardin Izmir.

An kuma ceto wasu karin bakin-hauren 67, wadanda jami'an tsaron Tekun Girka suka kora su zuwa ruwan Turkiyya na yankin Kusadasi da Didim da ke lardin Aydin na kasar Turkiyyar.

A wani bangaren na daban, tawagar jami'an tsaron gabar tekun sun ceto wasu bakin- haure 10, wadanda ke tafiya cikin wani kwale-kwalen da ke da matsala a gabar tekun gundumar Gomec da ke lardin Balikesir.

Turkiyya da kungiyoyin kare hakkin bil'adama na duniya sun sha yin Allah wadai da haramtaccen matakin kasar Girka na korar bakin-haure wadanda ke tafe ba bisa ka'ida ba.

Sun ce hakan ya saba wa ka'idojin jin-kai da dokokin kasashen duniya, suna masu cewa yin hakan na kara jefa rayuwar bakin-haure masu rauni ciki har da mata da kananan yara cikin hatsari

MAJIYA:TRT World