Turkiyya na ci gaba da ƙoƙarin hana bunƙasar 'yan ta'adda a arewacin Syria don kare kan iyakarta. Hoto: AA

Turkiyya ta "kawar" da ƴan ta'addar YPG/PKK fiye da 1,351 tun farkon wannan shekarar, ciki har da waɗanda suke ɓuya a faɗin kan iyakarta da Iraƙi da arewacin Syria, kamar yadda Ma'aikatar Tsaron Kasar ta bayyana.

"Jumullar ƴan ta'adda 80 aka kawar a makon da ya wuce," kamar yadda wani jami'in Ma'aikatar Tsaron Kasar ya shaida wa manema labarai a Ankara ranar Alhamis.

"Ana ci gaba da ƙoƙarin samar da zaman lafiya ba tare da ɓata lokaci ba a Syira, lamarin da zai ba da damar mayar da ƴan ƙasar yankuna masu aminci lami-lafiya," in ji jami'in, yana mai magana a kan ƙoƙarin Turkiyya na kare faɗaɗar ayyukan ta'addanci a iyakar kasar da Syria da kuma tabbatar da tsaron ƴan Siriyan.

An dauki dukkan matakan da suka dace wajen tabbatar da tsaro da zaman lafiya a yankunan da ake gudanar da samamen, kuma masu kai hare-haren ta'addanci sun gamu da gamonsu, jami'in ya ƙara da cewa.

Tun a watan Janairu ƙungiyar ta'addanci ta YPG/PKK ta kai hare-hare 342 a yankunan da Turkiyya ke yaƙi da ta'addanci, an kuma da "kawar" da ƴan ta'adda 991 ta hanyar martanin gaggawa da sojojin Turkiyya suka kai, a cewar jami'in.

Hukumomin Turkiyya na amfani da kalmar "kawarwa" ne don su nuna cewa ƴan ta'addar da ake magana a kai ko dai sun miƙa wuya ko an kashe su ko kuma an kama su.

'Daukan matakan da suka dace'

Da suke amsa wata tambaya da ta shafi rikici tsakanin ƙabilun Larabawa da ƙungiyoyin ta'addanci a arewacin Syria, majiyoyin ma'aikatar tsaro sun ce: "Muna ɗaukar dukkan matakan tabbatar da tsaron dakarunmu da ma'aikatanmu; babu wani abu marar daɗi."

Tun shekarar 2016, Ankara ta ƙaddamar da ayyuka uku na yaƙi da ta'addanci a faɗin iyakarta da arewacin Siriya don daƙile hana kafuwar ta'addanci da kuma samar da zaman lafiya ga mazauna yankin: ayyukan su ne Euphrates Shield (2016) da Olive Branch (2018), da kuma Peace Spring (2019).

A cikin fiye da shekara 35 da ta yi tana aiwatar da ayyukan ta'addanci a kan Turkiyya - ƙungiyar PKK - wacce Turkiyya da Amurka da Tarayyar Turai suka ayyana a matsayin ta ta'addanci, ta yi sanadin mutuwar mutum fiye da 40,000 da suka haɗa da mata da yara da kuma jarirai. Kungiyar YPG ita ce reshenta a Siriya.

Cibiyar sa ido ta Turkiyya da Rasha da ke Karabakh

Akan tambayar da ta shafi halin da ake ciki yanzu a yankin bayan ayyukan yaƙi da ta'addanci da rundunar sojin Azerbaijan ke yi a Karabakh da kuma ayyukan cibiyar sa ido ta Turkiyya da Rasha kuwa, majiyoyin sun ce suna sa ido sosai akan lamarin.

Cibiyar na ci gaba da ayyukanta kuma ba a gano wata alama ta take yarjejeniyar tsagaita wuta ba a yankin bayan ayyukan da rundunar sojin Azerbaijan ta ƙaddamar, in ji majiyoyin.

A makon da ya wuce ne, bayan da ƙungiyoyin mayaƙan sa kai na Armeniya a Karabakh suka yi wata takalar faɗa, sai Azerbaijan ta ce ta ƙaddamar da "ayyukan yaƙi da ta'addanci" a yankin, don jaddada yarjejeniyar zaman lafiya ta ƙasashe uku da aka cimma a shekarar 2020 tsakaninta da Rasha da Armeniya. Bayan awa 24 ne kuma aka ayyana tsagaita wuta.

Cibiyar, wacce aka samar da ita don sa ido a kan yarjejeniyar ta 2020, tana ci gaba da ayyukanta tun ranar 30 ga waran Janairun 2021.

AA