Ronaldo ya yi wa Real Madrid da Barcelona wasa a baya kafin ya koma Al Nassr. / Hoto: Getty Images

Christiano Ronaldo ya ce har yanzu akwai sauran kwallayen da zai ci a bana bayan ya ci kwallonsa ta 50 a 2023.

Ya bayyana haka ne bayan kungiyarsa ta Al Nassr ta ci Al Shabab 5-2 a gasar Cin Kofin Sarkin Saudiyya.

Tsohon dan wasan na Manchester United da Real Madrid ya ci kwallon a kusa da kusa da kafarsa ta dama a minti na 74.

“Babban nasara kuma ina farin cikin sanar da cin kwallota ta 50 a 2023,” kamar yadda dan wasan na Portugal mai shekara 38 ya rubuta a shafinsa na Instagram bayan kwallon tasa ta taimaka wa kulob din ya kai zagayen kusa da na karshe a ranar Litinin.

“Ina godiya da irin goyon bayan da na samu daga ‘yan kungiyata da magoya bayana da kuma iyalina! Akwai sauran damar cin wasu a bana.”

Dan wasan ya ci akalla kwallo daya a kusan duka wasan da ya buga wa kungiyar ta Al Nassr. Haka kuma ya ci kwallon goma ga Portugal a wasanni tara da ya buga a 2023.

TRT Afrika