Wasa 11 ne ya rage a kammala gasar Firimiya ta bana. / Hoto: AFP

Kocin Manchester City, Erik ten Hag ya dage kan cewa maƙwabtansu kuma manyan abokan hamayyarsu, Manchester City ba su fi su aji ba, duk da shan kashin da suka yi a wasansu na Lahadi da ci 3-1.

Erik Ten Hag ya yi wannan ikirari ne bayan da aka yi masa tambaya kan ko galabar da aka yi a kansu ta nuna cewa akwai wagegen bambanci na kwarewa tsakanin kungiyoyin biyu da ke birnin Manchester.

A kokarinsa na nuna rashin nasarar tawagarsa ba ya nufin Man City ta kere musu a aji, Ten Hag ya yi nuni kan 'yan wasansa da ke jinya, wadanda ba su samu damar buga wasan ba.

Ya kuma ayyana galabar da aka yi kansu a matsayin wata 'yar tazara, duk da cewa Man CIty ta nuna matukar rinjaye a kusan kowane bangare na wasan, tun lokacin da Marcus Rashford ya fara ciyo musu kwallo a farkon wasan.

A wasan dai, City ta kere su kusan a duka ma'aunin kwarewa, inda United ta rike kwallo da kaso na 27 kacal cikin 100 inda City take da kaso 73.

A yawan bugun kan raga United na da 1 CIty na da 8, a kwakkwaran bugu kuma, United na da 3 City na da 27.

A yawan taba kwallo ma, United na da 478, yayin da City ke da 981. Sai a fannin ba da kwallo United na da 305 inda City ke da fasin 801. Haka ma a yawan bugun kwana United ta buga 15, inda City ta buga 2 kacal.

Da yake ba da amsa kan kokarin 'yan wasansa, Ten Hag ya ce, "Za mu iya nuna bajinta, kuma mun nuna hakan a wasan karshe na gasar FA, amma dai ranar nan ta City ce, kar ku manta da wannan. Su ne kulob din da suka fi kowa a duniya a yanzu."

Sakamakon wasan nasu ya bar Man United a mataki na 6, yayin da CIty ke gaba da su da ratar maki 18, a mataki na 2 a teburin na FIrimiya. Dukkaninsu dai wasanni 11 ne suka rage musu kafin kammala gasar.

TRT Afrika