| Hausa
WASANNI
2 MINTI KARATU
CAF 2023: 'Yan Nijeriya Victor Osimhen da Asisat Oshoala sun lashe kyautar gwarazan 'yan kwallon Afirka
Osimhen, wanda yanzu shi ne zakaran kwallon kafar Italiya, ya doke dan wasan Liverpool da Masar Mohamed Salah da dan wasan Paris Saint-Germain da Maroko Achraf Hakimi inda ya lashe kyautar.
CAF 2023: 'Yan Nijeriya Victor Osimhen da Asisat Oshoala sun lashe kyautar gwarazan 'yan kwallon Afirka
'Yan Nijeriya Victor Osimhen da Asisat Oshoala sun lashe kyautar gwarazan 'yan kwallon Afirka na CAF 2023./Hoto: CAF / Others
11 Disamba 2023

'Yan Nijeriya Victor Osimhen da Asisat Oshoala sun lashe kyautar gwarazan 'yan kwallon Afirka na CAF 2023 a rukunin maza da mata a bikin da aka gudanar a Marrakech, babban birnin Maroko ranar Litinin da maraice.

Osimhen, wanda yanzu shi ne zakaran kwallon kafar Italiya, ya doke dan wasan Liverpool da Masar Mohamed Salah da dan wasan Paris Saint-Germain da Maroko Achraf Hakimi inda ya lashe kyautar.

Oshoala, mai shekara 29, tana cikn 'yan wasan Nijeriya mata da suka kai zagayen 'yan-goma-sha-shida a Gasar Kwallon Kafa ta FIFA da aka gudanar a bazara a kasashen Australia da New Zealand ko da yake Ingila ta fitar da su daga gasar.

Ta zama 'yar kwallon kafar Afirka ta farko da ta ci wasa a Gasar cin Kofin Duniya uku, a 2015 da 2019 da kuma bana.

Ga jerin sauran rukunan da suka samu nasara a wajen bayar da kyautar:

Gwarzuwar tawagar kwallon kafa ta kasa a rukunin maza - Maroko

Gwarzuwar tawagar kwallon kafa ta kasa a rukunin mata – Nijeriya

Gwarzon matashin dan wasa na shekara - Lamine Camira – Senegal

Gwarzuwar matashiyar 'yar wasa ta shekara - Nesryne El Chad - Maroko

Kulob da ya fi bajinta a shekara - Al Ahly - Egypt

MAJIYA:TRT Afrika